Mambobin APC sun yi zanga-zanga kan zaben fidda gwani a Katsina (hotuna)
Daruruwan magoya bayan jam’iyyar All Progressives Congress (APC) sun fito unguwannin jihar Katsina don yin zanga-zanga kan tsarin zaben fidda gwani.
Legit.ng ta tattaro cewa magoya bayan jam’iyyar sun gudanar da zanga-zanga cikin lumana a mazabar Dustinma/Kurfi kan gudanar da zaben fidda gwani na majalisar dokokin kasar ba bisa ka’ida ba a jihar.
Da suka kai mamaya sakatariyar APC a karamar hukumar Dutsinma, masu zanga-zangan sun ce wasu dake ji da kari mulki sun yi yadda suka ga dama a zaben.

Asali: Facebook
Masu zanga-zangan wanda suka hada da maza da mata sun kasance dauke da kwalayen sanarwa darubutu daban-daban kamar: “Muna bukatar adalci daga APC shiyar Dutsinma Kurfi”. “Honarable Dallami Muhammad Kurfi muke so a matsayin dan takararmu a zaben 2019, ba adalci ba kuri’a”.

Asali: Facebook
Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.naij.com
Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa
Ko a http://twitter.com/legitnghausa
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Asali: Legit.ng