Takarar Atiku: PDP ta bawa Saraki, Tambuwal da Dankwambo manyan mukamai

Takarar Atiku: PDP ta bawa Saraki, Tambuwal da Dankwambo manyan mukamai

Kwamitin yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa a karkashin jam'iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya amince da nadin shugaban majalisar dattijai, Bukola Saraki, a matsayin wanda zai jagoranci kamfen din Atiku a fadin Najeriya.

Kazalika kwamitin ya amince da nadin Aminu Waziri Tambuwal, gwamnan jihar Sokoto, a matsayin wanda zai jagoranci kamfen din Atiku a shiyyar arewa maso yamma.

Wannan sanarwar na kunshe cikin wata sanarwa da sakataren yada labaran jam'iyyar PDP, Kola Ologbondiyan, ya fitar.

Takarar Atiku: PDP ta bawa Saraki, Tambuwal da Dankwambo manyan mukamai
Takarar Atiku: PDP ta bawa Saraki, Tambuwal da Dankwambo manyan mukamai
Asali: UGC

DUBA WANNAN: Batan Janar Alkali: Mun gano fuskokin masu hannu cikin kisan sa - Hukumar Soji

Sanarwar ta ce "PDP ta nada Bukola Saraki, shugaban majalisar dattijai, a matsayin shugaban yakin neman zaben Atiku na kasa.

"Mai girma gwamnan jihar Sokoto, Aminu Waziri Tambuwal, zai jagoranci yakin neman zaben Atiku a yankin arewa maso yamma.

"Mai girma gwamnan jihar Gombe, Ibrahim Dankwambo, zai jagoranci kamfen din Atiku a yankin arewa maso gabas.

"Samuel Ortom, gwamnan jihar Benuwe zai zama Sarkin yakin kamfen din Atiku a yankin arewa ta tsakiya," kamar yadda sanarwar ta tabbatar.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin Legit.ng Hausa zai koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel