Rikicin APC a Zamfara: Shugaba Buhari na ganawa sirri a Gwamna Yari
- Shugaban Kasa Buhari ya gana da Gwamnan jihar Zamfara, Abdulaziz Yari
- Hakan ya biyo bayan rikicin APC da ya barke a jihar Zamfara
- Har yanzu dai an gaza fitar da dan takara na APC a jihar
Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a ranar Juma’a, 12 ga watan Oktoba ya yi ganawar sirri da Gwamna Abdulaziz Yari na jihar Zamfara a fadar shugaban kasa dake Abuja.
Kamfanin dillancin labaran Najeriya (NAN) ta ruwaito cewa Yari wanda ya ziyarci fadar shugaban kasar karo na biyu tun bayan da rikici ya barke a jihar Zamfara kan zaben fidda gwanin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ya samu rakiyar Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Ganduje.
NAN ta ruwaito cewa Yari yayi amfani da damar wajen sanar da Shugaba Buhari halin da ake ciki kar abubuwan dake faruwa a siyasar Zamfara lokaci da bayan zaben fidda gwanin APC wanda bai cimma nasara ba.
KU KARANTA KUMA: Yanzu Yanzu: Atiku na ganawar sirri da Peter Obi
Kwamitin da aka tura jihar Zamfara don gudanar da zaben fidda gwanin sun gaza gudanar da shirin inda suka bayyana matsalar tsaro a matsayin dalili.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin Legit.ng Hausa zai koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewar ku tare da mu.
Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng
Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa
Ko a http://twitter.com/naijcomhausa
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Asali: Legit.ng