Dan majalisar wakilai ya sake samun tikitin takara a PDP karo na 4 a Sokoto

Dan majalisar wakilai ya sake samun tikitin takara a PDP karo na 4 a Sokoto

Wani dan majalisar wakilai da ya shafe zango uku a majalisar, Isa Bashir-Kalanjeni ya sake samun tikitin jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) takarar kujerar mazabar Tangaza/Gudu a jihar Sokoto a zaben 2019.

Bashir-Kalanjeni, wanda ya kasance dan takara guda, ya zamo baida abokin hamayya a ranar Alhamis, 4 ga watan Oktoba.

Jami’in zaben, Malam Usman Yabo ne ya kaddamar da nasarar nasa bayan wakilai sun tabbatar da shi, kamfanin dillancin labarai ta ruwaito.

Dan majalisar wakilai ya sake samun tikitin takara a PDP karo na 4 a Sokoto
Dan majalisar wakilai ya sake samun tikitin takara a PDP karo na 4 a Sokoto
Asali: UGC

Yabo a wata sanarwa yace wakilan jam’iyyar 207 ne suka tabbatar da Bashir Kalanjeni a matsayin dan takara kamar yadda doka ta tanadar.

KU KARANTA KUMA: Gwamna Shettima ya lashe tikitin takarar sanata a APC

Da yake jawabin godiya Bashir-Kalanjeni ya yabama wakilai da sauran magoya bayan jam’iyyar kan goyon bayan da suka bashi, sannan yayi alkawarin yiwa mazabar shi hidima ta fannin lafiya, ilimi da sauransu.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin Legit.ng Hausa zai koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewar ku tare da mu.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel