Kaduna 2019: Isa Ashiru ya lashe zaben fidda gwani na PDP

Kaduna 2019: Isa Ashiru ya lashe zaben fidda gwani na PDP

- Isah Ashiru, ya doke sanata Suleiman Hunkuyi, Sani Sidi da tsohon gwamnan jihar Ramalan Yero a zaben fidda gwani na PDP

- Ya lashe zaben ne da kuri’u 1300 inda Sanata Hunkuyi ya sami kuri’u 565 shi kuma Sani Sidi ya samu kuri’u 560 sannan Ramalan y samu 36

Fitaccen dan siyasar nan kuma tsohon dan majalisar tarayya, Isah Ashiru, ya doke sanata Suleiman Hunkuyi, Sani Sidi da tsohon gwamnan jihar Ramalan Yero a zaben fidda gwani da aka yi a jihar Kaduna a karshen mako.

Isah Ashiru ya lashe zaben ne da kuri’u 1300 inda Sanata Hunkuyi ya sami kuri’u 565 shi kuma Sani Sidi ya samu kuri’u 560.

Kaduna 2019: Isa Ashiru ya lashe zaben fidda gwani na PDP
Kaduna 2019: Isa Ashiru ya lashe zaben fidda gwani na PDP
Asali: UGC

Tsohon gwamna Ramalan Yero ya samu kuri’u 36.

A daya bangaren kuma jimillan yayan jam’iyyar APC kuma wakilan da suka kada ma gwamnan jahar Kaduna Malam Nasir Ahmad El-Rufai kuri’u a zaben fitar da gwani na jam’iyyar APC na takarar gwamnan jahar, kamar yadda kamfanin dillancin labaru, NAN, ta ruwaito.

Majiyar Legit.ng ta ruwaito a ranar Lahadi, 30 ga watan satumba ne aka gudanar da wannan zabe a dandanlin Murtala dake garin Kaduna, inda wakilai dubu uku da dari bakwai da tamanin da biyu (3, 782) daga kananan hukumomi ashirin da uku suka kada kuri’a.

KU KARANTA KUMA: Yanzu Yanzu: Saraki da Dogara basu halarci faretin ranar yancin kai ba

Shugaban zaben, Mathew Idukriyekemwen ya tabbatar da nasarar Gwamna El-Rufai, inda yace gwamnan ya samu kuri’a 2447, yayin da aka samu gurbatattun kuri’u taaktin da uku (33), sai dai shugaban zaben bai bayyana matsayin kuri’u dubu daya da dari uku da biyu (1,302) da suka rage ba.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng