Zaben Osun: Saraki ya hadu da Omisore (hoto)

Zaben Osun: Saraki ya hadu da Omisore (hoto)

Shugaban maalisar dattawa, Bukola Saraki ya je Ile Ife inda ya hadu dan Sanata Iyiola Omisore dan takarar jam’iyyar Social Democratic Party (SDP) a zaben gwamna da aka gudnar a ranar Asabar da ya gabata.

Jam’iyyar PDP na yunkurin ganin takayar da jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki a zaben da za’a ake gudanarwa a ranar Alhamis mai zuwa.

Sanata Ademla Adeleke na PDP ya samu kuri’u 254, 698 inda yayima Gboyega Oyetola na APC zarra da kuri’u 353.

Zaben Osun: Saraki ya hadu da Omisore (hoto)
Zaben Osun: Saraki ya hadu da Omisore
Asali: Twitter

Daga cikin kullin da suke yi na samun kuri’un ja’iyyar SDP, Saraki ya gana da misore a ranar Litinin, 24 ga watan Satumba.

KU KARANTA KUMA: Zan marawa duk wanda ya samu tikitin takarar shugaban kasa a PDP baya – Sanata Mark

Koda dai ba’a bayyana cikakken bayanin abuna ganawar tasu ta kunsaba, an yi has ashen cewa baya rasa nasaba da zaben da za’a sake gudanarwa a ranar Alhamis, 27 ga watan Satumba.

A baya Legit.ng ta rahoto cewa daruruwan magoya bayan jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) a ranar Litinin, 24 ga watan Satumba sun mamaye hedkwatar hukumar zabe mai zaman kanta dake Osun don yin zanga-zanga akan sake zaben gwamna a jihar da hukumar tayi umurni.

Masu zanga zangar sun kasance da kwalayen sanarwa da rubutu daban-daban kasar “Babu sake zabe, “INEC kada ku hada kai da APC”; “Mutane sun yi Magana a ranar Asabar, ku sanar da sakamakon zabe” da dai sauransu.

Masu zanga-zangar su caccakin hukumar INEC kan kin kaddamar da Sanata Ademola Adeleke a matsayin wanda ya yi nasara a zaben baya ya samu adadin kuri’u mafi yawa

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng