Gabanin zabe, gwamna Elrufai zai biya malaman Kaduna kudaden da suke bin gwamnati

Gabanin zabe, gwamna Elrufai zai biya malaman Kaduna kudaden da suke bin gwamnati

- Gwamnatin jihar Kaduna zata biya sababbin malamai kudaden su

- An tabbatar da karatun yara mata kyauta a jihar

- An maida biyan albashin malamai SUBEB, maimakon karamar hukuma

Gabanin zabe, gwamna Elrufai zai biya malaman Kaduna kudaden da suke bin gwamnati
Gabanin zabe, gwamna Elrufai zai biya malaman Kaduna kudaden da suke bin gwamnati
Asali: Twitter

Gwamnatin jihar Kaduna tayi alkawarin biyan sababbin malamai duk kudin da suke bi nan da karshen watan satumba.

Kwamishinan ilimi na jihar, Ja'afaru Sani, ya fadi hakan a gurin horar da malaman firamare da akewa malaman akan Jolly Phonics teaching methodology wanda Universal Learning Solutions da hadin guiwar SUBEB reshen jihar Kaduna suka hada a ranar juma'a.

Yace an yanke shawarar biyan malaman kudin da suke bi ne bayan taron da sukayi da Gwamna Nasir Elrufai akan maganar a ranar litinin.

Gwamnan ya maida biyan albashin malamai SUBEB daga kananan hukumomin su.

Kwamishinan ya kara da cewa, gwamnan ya tabbatar da ilimin yara matan sakandaren jihar kyauta.

DUBA WANNAN: An biya 'yan NEPA kudadensu na bashi daga Tarayya

Yayi bayanin cewa gwamnatin jihar ta yanke shawarar cire duk wani abu da zai zama kalubale ga karatun mata a matsayin su na ginshikin al'umma.

Yace ma'aikatar su ta aikawa da ofisoshin yankunan jihar da makarantun sakandare umarnin tabbatar da ilimin kyauta

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel