Zainab Ahmed ministar kudi ce – Fadar shugaban kasa

Zainab Ahmed ministar kudi ce – Fadar shugaban kasa

- Fadar shugaban kasa ta sanar da cewa Zainab Ahmed zata yi aiki a matsayin ministar kudi ne kawai

- Kakakin shugaba Buhari, Femi ya bayyana cewa zata ajiye tsohuwar matsayinta na karamar ministar kasafi da tsare-tsaren kasa

- Zainab dai maye gurbin Kemi Adeosun ne bayan tayi murabus

Fadar shugaban kasa ta bayyana cewa Zainab Ahmed wacce aka dauko daga ma’aikatar kasafin kudi da tsare-tsare kasa zuwa ma’aikatar kudi bayan murabus din Misis Kemi Adeosun, zata bar matsayinta na baya.

Adeosun ta yi murabus a makon da ya gabata biyo bayan rade-radi cewa ta mallaki takardan NYSC dinta ba bisa ka’ida ba.

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ne ya mayar da Zainab Ahmed ma’aikatar kudi daga na kasafin kudi da tsare-tsare, inda zata yi jagoranci a matsayin ministar kudi.

Zainab Ahmed ministar kudi ce – Fadar shugaban kasa
Zainab Ahmed ministar kudi ce – Fadar shugaban kasa
Asali: Depositphotos

An samu sabanin ra’ayi kan ko zata hada matsayin biyu na ma’aikatar kasafin kudi da sabon matsayinta.

A wajen taron zaman majalisar zartarwa da aka gudanar a jiya, Laraba, 18 ga watan Satumba, Zainab ta zauna ne akan kujerar Adeosun a zangon majalisar.

KU KARANTA KUMA: Za a hukunta masu yi wa mata saki uku a lokaci guda a kasar Indiya

Da yake kwance kullin bayan taron FEC, kakakin shugaban kasa, Femi Adesina ya bayyana cewa Zainab zata ajiye tsohuwar mukaminta a matsayin karamar ministar kasafi, sannan zata zama shugabar ma’aikatar kudi, don haka matsayinta na yanzu shine ministar kudi.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng