Yadda zan kawo karshen rikicin makiyaya idan na zama shugaban kasa - Makarfi

Yadda zan kawo karshen rikicin makiyaya idan na zama shugaban kasa - Makarfi

- Daya daga cikin masu neman tikitin takarar shugabancin kasa a PDP, Sanata Makarfi ya ce akwai wadanda ke daukan nauyin kashe-kashe a Najeriya

- Makarfi ya ce zai kawo karshen kashe-kashen muddin aka zabe shi a matsayin shugaban kasa kamar yadda ya magance kashe-kashe a jihar Kaduna

- Makarfi ya ce zubar da jinin da ake a Najeriya tayi yawa, ya zama dole a kawo karshen lamarin

Tsohon shugaban riko na PDP, Sanata Ahmed Mohammed Makarfi, ya ce an gaza kawo karshen kashe-kashen da ke faruwa a wasu sassan Najeriya saboda akwai wadanda suka hada baki domin ingiza rikicin.

Sai dai ya yi alkawarin kawo karshen kashe-kashen muddin ya samu tikitin takarar PDP kuma aka zabe shi a matsayin shugaban kasa.

Yadda zan kawo karshen rikicin makiyaya idan na zama shugaban kasa - Makarfi
Yadda zan kawo karshen rikicin makiyaya idan na zama shugaban kasa - Makarfi
Asali: Twitter

Tsohon gwamnan na jihar Kaduna, ya yi wannan furucin ne a ranar Juma'a yayin da ya tafi mayar da fam din takarar shugabancin kasar sa a ofishin PDP da ke Abuja.

DUBA WANNAN: Kanin Dankwambo ya fasa komawa APC, ya bayar da dalili

Makarfi ya ce zai maimaita abinda ya yi lokacin da ya ke gwamna a Kaduna na kawo karshen kashe-kashe a jihar tsakanin kabilu da mabiya addinai daban-daban.

"Ba zai taba yiwuwa kashe-kashen nan su cigaba da faruwa ba face akwai hadin bakin wasu mutane a kasar. Masu makircin zasu iya kasancewa daga kowanne bangare na kasar amma babu yadda za'ayi abubuwa su cigaba da faruwa haka ba tare da hadin baki ba."

"Idan aka zabe ni a matsayin shugaban kasa, zanyi amfani da kwarewata domin kawo karshe kashe-kashen kamar yadda nayi lokacin ina gwamna a jihar Kaduna. Wannan ba shaci-fadi bane saboda na yi shi a aikace," inji Makarfi.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164