An gurgunta Boko Haram, babu wasu yan ta’adda dake sake kafuwa a arewa maso gabas - Buratai

An gurgunta Boko Haram, babu wasu yan ta’adda dake sake kafuwa a arewa maso gabas - Buratai

Shugaban hafsan sojin Najeriya, Laftanar Janar Tukur Buratai a ranar Talata, 3 ga watan Satumba ya sake bayyana cewa an gurgunta yan ta’addan Boko Haram sannan kuma cewa babu yan ta’adda dake sake kafuwa a Arewa maso gabashin kasar kamar yadda ake rade-radi.

Buratai, wadda yayi Magana a Jaji wajen yaye runduna 55 na musamman yace “a rayuwa, dole mutun ya fuskanci wasu kalubale.”

Kamfanin dillancin labaran Najeriya (NAN) ta rahoto cewa a yan kwanakin da suka gabata, akwai rahoton labarai dake cewa yan ta’adda sun kai hari ga sojoji a yankin arewa maso gabas inda akayi ikirarin cewa an kashe wasu sojoji.

Sai dai rundunar sojin ta karyata harin da kuma cewar ta rasa jami’anta.

An gurgunta Boko Haram, babu wasu yan ta’adda dake sake kafuwa a arewa maso gabas - Buratai
An gurgunta Boko Haram, babu wasu yan ta’adda dake sake kafuwa a arewa maso gabas - Buratai
Asali: Depositphotos

Buratai yaje Jaji netare da rakiyan babban hafsan sojin Afrika ta Kudu, Laftanar Janar Lindile Yam wadda ya kawo ziyara kasar.

KU KARANTA KUMA: Dubi Ronke Ajayi wacce ta sha alwashin siyar da dukkanin abunda ta mallaka don siyawa Buhari fam din takara

A baya Legit.ng ta rahoto cewa Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa babu wani yanki a kasar dake karkashin ikon yan ta’addan Boko Haram a yanzu.

Ya bayyana hakan a ranar Lahadi, 2 ga watan Satumba, a Beijing, kasar China yayinda yake bayyana wasu nasarori da gwamnatinsa ta samu a lokacin da yake jawabi ga ‘yan Najeriya mazauna kasar.

Shugaban kasar ya danganta nasarorin ga ayyukan da hukumomin tsaro suka gudanar wajen yakar ta’addanci a yankin arewa maso gabashin kasar.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel