An nada sabon jakadan Najeriya a birnin New York

An nada sabon jakadan Najeriya a birnin New York

- Ya maye gurbin tsohon jakadan ne wanda ya rasu ranar Lahadi.

- Yayi alkawarin kawo cigaba a bangaren jakadancin Nageriya.

An nada sabon jakadan Najeriya a birnin New York
An nada sabon jakadan Najeriya a birnin New York

Benaoyagha Okoyen ya karbi aiki a matsayin karamin jakadan Najeriya a birnin New York.

Okoyen dai ya maye gurbin tsohon jakada Mr Tanko Suleiman wanda ya rasu a ranar Lahadi bayan kwanaki kadan bayan dawowar sa daga rangadi a birnin na New York, inda yayi ritaya a 27 ga watan Afrilun da ya gabata.

DUBA WANNAN: Wata duniya zata sakko kusa da tamu ranar 31 ga wannan watan - NASA

Sabon jakadan Najeriyan ya taba aiki da ofishin jakadanci na birnin New York a shekarar 2015.

Okoyen yayi alkawarin kawo cigaba a bangaren jakadancin ga 'yan Najeriya.

Ya tabbatar da kawo gagarumin cigaba akan yanda ake bida 'yan Najeriya a ofishin jakadancin.

Okoyen yana fatan cimma hakan ta hanyar zaunawa da kwararru a ofishin jakadancin dan kawowa Najeriya canji.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel