Yanzu Yanzu: Ana nan ana tattara sa hannu don tsige shugaba Buhari a yanzu haka – Dan majalisa

Yanzu Yanzu: Ana nan ana tattara sa hannu don tsige shugaba Buhari a yanzu haka – Dan majalisa

Wani dan majalisar wakilai Muhammed Gudaji Kazaure, yayi zargin cewa ana nan ana shirya makirci don tsige shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Vanguard ta rahoto cewa dan majalisar wanda keda kusanci da shugaba Buhari a majalisar ya bayyana hakan a ranar Talata, 5 ga watan Yuni bayan ganawar sirri na sa’o’i 3 tsakanin majalisar dattawa da na wakilai.

Yayi ikirarin cewa an tattara sa hannu domin tsge shugaban kasar amma yana da tabbacin cewa barazanar ba zai cimma nasara ba saboda wadanda ke bayan shugaban kasar suna da yawa.

Yanzu Yanzu: Ana nan ana tattara sa hannu don tsige shugaba Buhari a yanzu haka – Dan majalisa
Yanzu Yanzu: Ana nan ana tattara sa hannu don tsige shugaba Buhari a yanzu haka – Dan majalisa

KU KARANTA KUMA: Kalli yadda ake rabon abinci karkashin tsarin ciyar da yara na gwamnatin tarayya a wata makarantar firamarin Jihar Kano

Kazaure yace shi baya goyon bayan abunda ya bayyana a matsayin makirci don tsige shugaban kasar idan yaki amincewa da sharudan da aka gindaya.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng