Madallah: Gwamnatin Tarayya ta bayyana adadin Kudade na rarar Ma'aikatan Bogi

Madallah: Gwamnatin Tarayya ta bayyana adadin Kudade na rarar Ma'aikatan Bogi

A ranar talatar da ta gabata ne shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana adadin kudade da gwamnatin sa ta samu na rara ma'aikatan bogi cikin ma'aikatun gwamnati wanda a halin yanzu ta adana inda za a ci moriyarsu a wani bangaren.

Kamar yadda jaridar The Nation ta ruwaito, shugaba Buhari ya bayyana cewa kimanin sama da N120bn gwamnatin sa ta samu na rara bayan ta rairaye ma'aikatan bogi a kasar nan daga ma'aikatun gwamnati.

Shugaba Buhari ya kuma bayyana cewa, gwamnatin sa ta samu rara ta N108bn a halin yanzu sakamakon asusun gwamnatin na bai-daya da gwamnatin sa da kaddama wanda a da can kudaden suke shigewa asusun bankunan kasar nan.

Ma'aikatan Boge: Gwamnatin Tarayya ta bayyana adadin Kudaden da ta ke asara
Ma'aikatan Boge: Gwamnatin Tarayya ta bayyana adadin Kudaden da ta ke asara

Legit.ng ta fahimci cewa, shugaba kasar ya bayyana hakan yayin bikin bayar da lambar yabo ga macancanta kawo ci gaban kasa a gwamnatin sa wadda ya hadar har da shugaban ma'aikatan gwamnatin tarayya, Winifred Oyo-Ita.

KARANTA KUMA: Hadimin Shugaba Buhari ya mayar da martani ga Hadimin Jonathan

Shugaban kasar ya kuma bayyana cewa, tsare-tsaren da gwamnatin sa ta gindaya sun rage hauhawar farashi da kimanin kaso 12.5 cikin 100.

Ya kara da cewa, matsin tattali arziki da kasar nan ta afka a shekarar 2016 da ta gabata a sakamakon dogaro da man fetur da kuma wawuson asusun gwamnati babu sassauci.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Domin shawara ko buƙatar bamu labari, tuntuɓe mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku duba shafukanmu na dandalin sada zumunta a:

https://facebook.com/naijcomhausa

https://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel