Al’umman Jihar Neja su na cabawa a Gwamnatin APC

Al’umman Jihar Neja su na cabawa a Gwamnatin APC

Mun samu labarin irin alherin da Jihar Neja da ke Arewa ta tsakiyar Najeriya ta samu a Gwamnatin Shugaban kasa Muhammadu Buhari. Abdul-Baqi Ebbo wanda yana cikin Mukarraban Gwamnan Jihar Neja ya bayyana wannan.

Al’umman Jihar Neja su na cabawa a Gwamnatin APC
Mutanen Jihar Neja sun ga aiki a Gwamnatin APC

Ayyukan da Gwamnatin Tarayya ta ke yi a Jihar Neja sun hada da aikin titi da na gada da dai sarau su. Daga cikin ayyukan dai da ake yi yanzu haka ko kuma ake shirin yi akwai:

KU KARANTA: Kayode Fayemi zai kara tsayawa takarar Gwamna a Ekiti

1. Ana fadada hanyar Suleja zuwa Garin Minna

2. Ana gina titin Garin Agaie zuwa Garin Baro

3. Ana gina gadar Tatabu

4. Ana gyara hanyar Kwantagoro zuwa Garin Makera

Bayan nan kuma an bada wasu sababbin kwangila 2 a Jihar:

5. Za a gyara hanyar Rijau tun daga Garin Kontogora

6. Za a gyara hanyar Garin Lambata zuwa Lapai

Haka zalika Gwamnatin Buhari na wani aikin na:

7. Yasan tashan ruwan Baro a Jihar ta Neja.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel