An karbe manyan bindigogi sama da 100 a hannu bata-gari a Neja

An karbe manyan bindigogi sama da 100 a hannu bata-gari a Neja

- Jami’an tsaro sun yi ram da masu kera mugayen makamai a Jihar Neja

- An yi nasarar karbe bindigogi sama da 100 da kuma harsahi kimanin 80

- Gwamnatin Shugaba Buhari na yaki da masu safarar migayun makamai

Mun samu labari cewa Jami’an tsaron ‘Yan Sandan Najeriya sun gano inda ake kera mugayen makamai a wani Kauye mai suna Mashegu a cikin Jihar Neja inda yanzu har an shiga Kotu.

An karbe manyan bindigogi sama da 100 a hannu bata-gari a Neja
'Yan Sanda sun karbe makamai a cikin Jihar Neja

Kamar yadda labari yake zuwa mana daga Jaridar Punch Jami’an ‘Yan Sandan kasar nan sun kama wasu da ake zargi da laifin kera mugayen makamai a Najeriya. Yanzu haka an maka su Kotu domin su zama darasi ga jama’a.

KU KARANTA: Jama’an Zakzaky sun cika tituna da zanga-zanga a Najeriya

Rundunar ‘Yan Sandan kasar kamar yadda Kakakin su na Yankin Jihar Neja Muhammad Abubakar ya bayyana sun karbe bindigogi sama da kala 100 da harsashi iri-iri. Yanzu dai ana cigaba da yakar miyagu a kasar.

A baya dai Sufetan ‘Yan Sandan kasar Ibrahim K. Idris ya haramta amfani da duk wasu makaman da aka kera ba bisa doka ba. A dalilin haka ne ake samun yawitar hare-hare iri-iri a Yankuna da dama na kasar irin su Benuwe da Taraba.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel