Jam'iyyar PDP ta baiwa Ummi Zeezee babban mukami

Jam'iyyar PDP ta baiwa Ummi Zeezee babban mukami

Rahotanni sun kawo cewa babban jam’iyyar adawan Najeriya, PDP ta baiwa tsohuwar jarumar fina-finan Hausa na Kannywood, Ummi Zeezee babban mukami.

An bata mukamin shugabar riko ta mata ta kungiyar dake yiwa PDP kamfe gida-gida ta kasa baki daya.

Ummi da take bayyana hakan a shafinta na sada zumunta da muhawara tace ta godewa Allah da wannan mukami da ta samu yau, kuma tana fatan Allah ya baiwa jam'iyyar ta PDP mulki a zaben shekarar 2019.

Jam'iyyar PDP ta baiwa Ummi Zeezee babban mukami
Jam'iyyar PDP ta baiwa Ummi Zeezee babban mukami

Ummi dai tayi suna wajan caccakar gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari.

KU KARANTA KUMA: Kalli hotunan yadda dandalin taro na Eagles Square ya cika ya tunbatsa sakamakon Maulidin Sheikh Ibrahim Nyass

Hakazalika shugaban kungiyar yiwa PDP kamfen gida-gida na kasa, Ibrahim Dahiru Danfulani ya tabbatar da wannan mukami na Ummi Zeezee a jiya Juma'a.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel