An kuma kashe mutane 5 a wani sabon rikici a Jihar Benuwe

An kuma kashe mutane 5 a wani sabon rikici a Jihar Benuwe

- Makiyaya sun hallaka mutane akalla 5 a wani gari a Benuwe

- An yi wa mutanen Garin Umenga kwantan-bauna ne a hanya

- Duk da Jami’an Sojin da aka kawo ba a fasa wannan ta’adi ba

Kwanan nan an kuma kashe mutane 5 a wani sabon harin da aka kai a Jihar Benuwe bayan da wasu Makiyaya su ka dura Garin Umenga. Jami’an Gwamnatin na Jihar Benuwe sun tabbatar da wannan hari yanzu haka.

An kuma kashe mutane 5 a wani sabon rikici a Jihar Benuwe
An kara kai hari a Banuwe yayin da ake sa ran zuwan Buhari

Labari ya zo mana daga Vanguard cewa an hallaka akalla mutum 5 bayan da wasu da ake zargi Makiyaya ne su ka kai hari a Karamar Hukumar Guma duk da Jami’an tsaron da aka baza domin kawo tsanaki a Yankin.

KU KARANTA: Shehu Sani ya kuma caccakar Gwamnatin Shugaba Buhari kan tsaro

Ba wannan ne karo na farko da aka kai hari wannan Gari ba don kuwa a farkon shekarar nan an yi kokarin hallaka mutanen da ke wannan Gari sai dai an tsaga da ragowar kwana. Wannan karo dai Makiyayan sun yi barna.

Mutum 1 ne kurum ya tsere ya kuma yi rai cikin wadanda aka kai wa harin kamar yadda mu ka ji. Ana zargin Makiyayan sun yi kwantan-bauna ne inda su ka budawa mutanen Garin wuta yayin da su ke hanyar komawa gidajen su.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Online view pixel