An kuma kashe mutane 5 a wani sabon rikici a Jihar Benuwe
- Makiyaya sun hallaka mutane akalla 5 a wani gari a Benuwe
- An yi wa mutanen Garin Umenga kwantan-bauna ne a hanya
- Duk da Jami’an Sojin da aka kawo ba a fasa wannan ta’adi ba
Kwanan nan an kuma kashe mutane 5 a wani sabon harin da aka kai a Jihar Benuwe bayan da wasu Makiyaya su ka dura Garin Umenga. Jami’an Gwamnatin na Jihar Benuwe sun tabbatar da wannan hari yanzu haka.
![An kuma kashe mutane 5 a wani sabon rikici a Jihar Benuwe An kuma kashe mutane 5 a wani sabon rikici a Jihar Benuwe](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt7er0cmr9b65.jpeg?v=1)
Labari ya zo mana daga Vanguard cewa an hallaka akalla mutum 5 bayan da wasu da ake zargi Makiyaya ne su ka kai hari a Karamar Hukumar Guma duk da Jami’an tsaron da aka baza domin kawo tsanaki a Yankin.
KU KARANTA: Shehu Sani ya kuma caccakar Gwamnatin Shugaba Buhari kan tsaro
Ba wannan ne karo na farko da aka kai hari wannan Gari ba don kuwa a farkon shekarar nan an yi kokarin hallaka mutanen da ke wannan Gari sai dai an tsaga da ragowar kwana. Wannan karo dai Makiyayan sun yi barna.
Mutum 1 ne kurum ya tsere ya kuma yi rai cikin wadanda aka kai wa harin kamar yadda mu ka ji. Ana zargin Makiyayan sun yi kwantan-bauna ne inda su ka budawa mutanen Garin wuta yayin da su ke hanyar komawa gidajen su.
Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng
Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa
Ko a http://twitter.com/naijcomhausa
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Asali: Legit.ng