Lamido ya tarbi masu sauya sheka zuwa PDP 5000 a Jigawa, ya sha alwashin kayar da Buhari a 2019
- Alhaji Sule Lamido, tsohon gwamnan jihar Jigawa da jam’iyyar PDP sun sha alwashin kayar da shugaba Buhari a 2019
- Ya ce kudirinsa kudirin Allah ne sannan kuma ya bukaci mutane da kadda sun yi kokarin tokare shi
- Lamido ya kuma ce an azabtar da shi tare da kai shi gidan yari saboda hasashensa na son ganin an yada damokradiyya a kasar
Alhaji Sule Lamido, tsohon gwamnan jihar Jigawa sannan kuma dan takarar shugabancin kasa a jam'iyyar PDP yayinda yake tarban sama da mutane 5,000 da suka sauya sheka daga APC zuwa PDP ya sha alwashin kayar da shugaban kasa Muhammadu Buhari a zaben 2019 idan har jam'iyyarsa ta basa tikitin takarar shugabancin kasa.
A ranar 17 ga watan Fabrairu, tsohon gwamnan a wani gangamin siyasa yayinda yake kaddamar da ofishin neman zabensa a karamar hukumarsa ta Birnminkudu dake jihar.
Da yake bayyana kudirinsa a matsayin al'ajabi, Lamido ya kalubalanci duk wanda ke mulki daga shugaban kasa har zuwa kasa da kadda suyi yunkuri hana Allah ikonsa, jaridar Independent ta rahoto.

Asali: UGC
Tsohon gwamnan ya kuma kalubalanci Buhari da ya fassara wasu yan zantuka da yayi a harshen Fulatanci a taron.
KU KARANTA KUMA: Hadimin gwamnan jihar Katsina ya kashe yarsa da mota
Lamido ya kuma yi ikirarin cewa Buhari da APC sun fada ma yan Najeriya karairayi a zaben 2019.
A baya Legit.ng ta rahoto cewa wani abun bakin ciki ya faru a ranar Juma’a a jihar Katsina lokacin da mai ba Gwamna Aminu Masari shawarar na musamman akan al’amuran addini, Abdullahi Darma, ya take yarsa, A isha da mota bisa tsautsayi.
Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng
Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa
Ko a http://twitter.com/naijcomhausa
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Asali: Legit.ng