Mun gana da shugaba Buhari ne domin yaba masa bisa nada Tinubu da yayi a matsayin mai sulhu – Gwamnonin APC

Mun gana da shugaba Buhari ne domin yaba masa bisa nada Tinubu da yayi a matsayin mai sulhu – Gwamnonin APC

- Gwamnonin APC sun bayyana kudirinsu na zuwa Daura

- Shugaban gwamnonin APC, Gwamna Rochas Okorocha na Imo, ya karyata rahotannin cewa sun kai ziyarar ne domin sanya shugaban kasar sake neman takara

- Okorocha ya kara da cewa gwamnonin APC sunyi amfani da damar wajen yaba ma Buhari bisa nada Asiwaju Bola Tinubu a matsayin mai sulhunta rigingimu a tsakanin yan jam’iyya

Gwamnonin APC a ranar Juma’a sunce kudirinsu na zuwa Daura jihar Katsina shine domin suyi ma shugaban kasa Muhammadu Buhari ta’aziyan rashin yan uwansa guda biyu da yayi.

Shugaban gwamnonin APC, Gwamna Rochas Okorocha na Imo, ya bayyana hakan lokacin da yake amsa tambayoyi daga manema labarai bayan wata ganawar sirri tare da shugaban kasa Buhari a gidansa na Daura a ranar Juma’a.

Ya karyata rahotannin cewa sun kai ziyarar ne domin sanya shugaban kasar sake neman takara.

Mun gana da shugaba Buhari ne domin yaba masa bisa nada Tinubu da yayi a matsayin mai sulhu – Gwamnonin APC
Mun gana da shugaba Buhari ne domin yaba masa bisa nada Tinubu da yayi a matsayin mai sulhu – Gwamnonin APC

Ya ce gwamnonin APC sunyi amfani da damar wajen yaba ma Buhari bisa nada Asiwaju Bola Tinubu a matsayin mai sulhunta rigingimu a tsakanin yan jam’iyya.

KU KARANTA KUMA: Ba a ga Ortom, Ambode, da Amosun ba yayinda gwamnonin APC suka isa Daura domin ziyartan Buhari

Idan bazaku manta ba a makon da ya gabata ne shugaban kasar ya nada Tinubu a matsayin mai sasanta yan jam’iyya.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng