2019 : Kashim Shettima yana kokwanton neman kujerar sanata

2019 : Kashim Shettima yana kokwanton neman kujerar sanata

- Kashim Shettima yace wasu mambobin jam’iyyar APC suna hura masa wuta ya nemi kujeran sanata

- Shettima ya karyata jita jita zama mataimakin shugaban kasa da ake ta yadawa

Kwanakin kadan bayan ya fito a gidan Talabijin yace ba zai tsaya takara a zaben 2019 ba, gwamnan jihar Borno, Kashim Shettima, yace wasu mambobin jam’iyyar APC suna hura masa wuta ya nemi kujeran sanata.

A wata hira da yayi da, Osasu Igbenidion, a gidan talabajin din AIT, Shettima ya fada mata cewa ba zai kara tsaya takara ba a lokacin da ta tambaye mai zai yi idan ya kamala wa’adin sa na gwamna.

2019 : Kashim Shettima yana kokwanton neman kujerar sanata
2019 : Kashim Shettima yana kokwanton neman kujerar sanata

Gwamnan Kashim Shettima ya ce zai je ya karo karatu idan ya sauka daga mulki, zai yi digiri a yaren Faransa.

KU KARANTA : Shittu ya zargi Ajimobi da nuna bangaranci da raba kawunan yan APC a jihar Oyo a wasikar da ya rubutawa Buhari

Kafin yanzu, ana ta yada jita-jita cewa, Kashima Shettima, zai ma mataimakin shugaban kasa idan Buhari ba zai tsaya takara ba a 2019.

Amma gwamnan ya karyata wannan zargi inda yace damuwar sa shine ya ga mutanen sa suna cikin zaman lafiya.

Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Asali: Legit.ng

Tags:
Online view pixel