Hukumar USAID ta kaddamar da shirin da zai bunkasa harkar noman masara a Kaduna

Hukumar USAID ta kaddamar da shirin da zai bunkasa harkar noman masara a Kaduna

- Hukumar USAID ta kafa wani shiri da zai bunkasa harkar noman masara a Kaduna

- Shirn zai tallafawa manoma 20,000 wanda ya kunshi mata a ciki

- Shirin zai taimaka wajen rage talaucin da manoma ke fuskanta

A cikin kokarin inganta harkar noma da take taimakawa wajen tattalin arzikin kasa, hukumar USAID tare da hadin gwiwar kamfanin Nestle na Najeriya sun kaddamar da tsarin ‘Ciyar da Najeriya a gaba da samar da ingatacciyar masarar Nestle' a jihar Kaduna.

Sunan mai taken 'samar da ciyarwa a gaba' na gwamnatin Amirka ne na yaki da cutar yunwa da samar da tsaro a duniya.

Hukumar USAID ta kafa wani shiri da zai bunkasa harkar nomar masara a Kaduna
Hukumar USAID ta kafa wani shiri da zai bunkasa harkar nomar masara a Kaduna

Domin kalubalen da ake fuskanta wajen noman masara da rashin samin riba musamman a noman masara da waken soya, hukumar USAID, kamfanin Nestle tare da hadin gwiwar wasu kamfanonin suka kafa wannan shiri.

Shirin zai samar da horo ga manoma, da kananan ma’aikatan noma a jihar Kaduna, manoman zasu koyi yadda za a rage gurbatattun iri don samin bunkasa a masara da waken soya ingatattu wanda zai samar da lafiya ingatacciya a cikin al’umma.

Shirin zai kuma taimakawa manoma sama da 20,000 wanda ya kunshi mata da yawa da masu sana’a a jihar.

DUBA WANNAN: Wata cikin 'yan Chibok da aka ceto daga Boko Haram ta zayyana sirrin kungiyar dalla-dalla

Darakta na hukumar USAID, Stephen Haykin ya bada sanarwar yadda shirin zai tallafawa kananan manoma da fitar da su daga kangin talauci

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng

Tags: