Gasar zakarun turai: Yau za'a raba jadawalin kungiyoyin da zau fafata

Gasar zakarun turai: Yau za'a raba jadawalin kungiyoyin da zau fafata

A yau ranar Alhamis din nan ne dai za'a rarraba jadawalin kunyiyoyin da za su fafata a cikin gasar kwallon kafa ta zakarun turai ta karar wasannin ta 2017/2018 wanda za'a gudanar a garin Monaco.

Kamar kuma dai yadda aka saba, al'adar gasar shine babu kungiyar da za ta kara da wadda take kasa daya a wasannin rukuni, yayin da kuma ko wace shekara mahukunta za su sanar da yadda za a raba kungiyoyin.

Gasar zakarun turai: Yau za'a raba jadawalin kungiyoyin da zau fafata
Gasar zakarun turai: Yau za'a raba jadawalin kungiyoyin da zau fafata

Legit.ng ta samu kuma cewa da zarar an rarraba jadawalin ake sa ran fara buga wasannin a cikin rukunonin tsakanin 12 da kum 13 ga watan Satumbar wannan shekarar yayin da kuma za'a yi wasan karshe a watan Mayun shekarar 2018 a Kyiv.

Haka ma dai kuma a lokacin rarraba jadawalin ne dai za a sanar da gwarzon danwasan da ya lashe kyautar gwarzon dan kwallon kafa da babu kamarsa a Turai a shekarar nan da sauran kyaututtuka da dama.

Kungiyar Real Madrid ce ke rike da kofin Zakarun Turai na 2016/17 na 12 da ta dauka jumulla.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng