Jami'an tsaron Najeriya sun kama mutane 6 masu hako zinare ta haramtacciyar hanya a Arewa

Jami'an tsaron Najeriya sun kama mutane 6 masu hako zinare ta haramtacciyar hanya a Arewa

Jami'an rundunar hukumar tsaron nan ta al'ummar farar hula watau Civil Defence a turance ta bayar da sanarwar kama wasu gungun mutane da take zargi da laifin hakar ma'adanin zinare ta haramtacciyar hanya a karamar hukumar Minna babban birnin jihar Neja.

Kwamandan rundunar ta jami'an tsaron na Sibil defence a jihar mai suna Mista Philip Ayuba shene ya shaidawa yan jarida hakan a ofishin sa dake a hedikwatar rundunar a kan titin tunawa da marigayi Mandela a Minna din.

Jami'an tsaron Najeriya sun kama mutane 6 masu hako zinare ta haramtacciyar hanya a Arewa
Jami'an tsaron Najeriya sun kama mutane 6 masu hako zinare ta haramtacciyar hanya a Arewa

Legit.ng ta samu kuma cewa hukumar tasu tana da alhaki akan dukkan yan Najeriya da su tabbatar da bin doka da oda sannan kuma ya bayyana kamasu a matsayin anunda ya yazama dole don samun ingattacen tsaro ga alummar yankin.

Daga karshe kuma kwamandan rundunar dai Mista Ayuba yace da zarar sun gama binciken su to tabbas za su turasu wadanda take zargin kotu domin shari'a.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng