Sheikh Dahiru Bauchi ya jagoranci kafa majalisar koli ta malamai na darikar Tijjaniyya a Najeriya

Sheikh Dahiru Bauchi ya jagoranci kafa majalisar koli ta malamai na darikar Tijjaniyya a Najeriya

Shehu Usman Dahiru Bauchi ya yi jagora ga manyan yan darikar Tijjaniya wadanda suka hada da Shehunai, Khalifofi, Muqaddamai da sauran mabiya darikar baki daya.

An dauki kwanaki biyu ana gudanar da taron a garin Bauchi, wato a ranakun Jumaá da Asabar.

Manyan Shehunnai, Khalifofi da Mukaddamai sun halarci wannan gagarumin taro da mabiya darika suka shirya.

Anyi kira ga mabiya Darika da su kaunaci junansu, su so junansu, su dunga ziyartar juna, sannan kuma suyi biyayya ga juna, kuma kowa ya amince cewa daga yanzu za’a dinga magana da murya bai daya ne.

Sheikh Dahiru Bauchi ya jagoranci kafa majalisar koli ta malamai na darikar Tijjaniyya a Najeriya
Sheikh Dahiru Bauchi ya jagoranci kafa majalisar koli ta malamai na darikar Tijjaniyya a Najeriya

KU KARANTA KUMA: Majalisar dokoki na ma shugaba Buhari adduán dwowa lafiya – Shehu Sani

Kuma wadanda suka samu halarta su sanarwa wadanda ba su zo ba. Daga karshe, takardar sakamakon taro za’a rarraba shi ga dukkan Zawiyyoyi.

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a email dinmu na labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng