Bahaushe mai ban haushi: Kazamin rikici ya barke tsakanin al'ummar Hausawa 2 a Legas

Bahaushe mai ban haushi: Kazamin rikici ya barke tsakanin al'ummar Hausawa 2 a Legas

Labaran da muke samu da dumi dumin su na nuni da cewa yanzu haka dai wani kazamin rikici ya barke a jihar Legas a babbar kasuwar nan ta safarar kayayyaki ta Alabarago a tsakinin bangarori biyu na jama'ar Hausawa mazauna yankin.

Yanzu haka ma dai wasu rahotannin daga jihar na cewa an ruga da mutune takwas zuwa asibiti wadanda aka ji wa rauni a lokacin bata kashin.

Bahaushe mai ban haushi: Kazamin rikici ya barke tsakanin al'ummar Hausawa 2 a Legas
Bahaushe mai ban haushi: Kazamin rikici ya barke tsakanin al'ummar Hausawa 2 a Legas

Legit.ng ta samu labarin cewa musababbin rikicin dai baya rasa nasaba da kokarin da ake yi na a sasanta tsakanin wasu bangarori biyu da ke zaune a kasuwar da basa jituwa da juna a kan shugabancin na kasuwar.

Haka ma dai majiyar ta bi ta ayyana cewa tuni dai har mahukunta a jihar sun tura jami'an tsaro na 'yan sanda zuwa yankin. Haka zalika kuma har yanzu 'yan sanda ba su ce komai ba kan batun.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng