Masu sana'ar karuwanci 72 sun shiga hannu a jihar Benuwe

Masu sana'ar karuwanci 72 sun shiga hannu a jihar Benuwe

Wata kungiyar mata ta yi zanga-zanga a jihar Benuwe don bayyana kukan ta akan al'amarin yawaitar yiwa kananan yara fyade a jihar wanda sanaiyar haka ne gwamnatin ta cafke ma su sana'ar karuwanci har 72 a jihar.

A daren ranar Alhamis din da ta gabata ne gwamnatin jihar Benuwe tare da hadin gwiwar 'yan sandan jihar suka kai simame gidajen karuwai 5 wanda su ka cafke kimanin guda 72 a birnin Makurdi.

Wannan kamen na karuwai ya bayu ne sanadiyar da wata kungiyar mata su ka nuna kukan su da yin zanga-zanga a kan yadda yiwa kananan yara fyade da lalata su yake karuwa a jihar.

Shugaban mai baiwa gwamntin jihar shawara a kan harkokin tsaro, Col, Edwin Jando ya bayyanawa wannan kungiyar ta mata cewa gwamnatin gwamna Samuel Ortom ba za ta lamunci wannan gurbatanci da yake faruwa a jihar ba.

Masu sana'ar karuwanci 72 sun shiga hannu a jihar Benuwe
Masu sana'ar karuwanci 72 sun shiga hannu a jihar Benuwe

Jando ya ce yunkurin da gwamnatin jihar ta ke wajen kawar da faruwar fitintinu a jihar ne ya sa suka cafke wannan karuwai a gidajen sana'ar su.

KU KARANTA: Hanyoyin kauce wa ambaliyar ruwa a Najeriya

Shugabar kungiyar ta mata ma su zanga-zanga, Magdalene Gbazua ta ce, kungiyar ta su ta yi wannan abu ne saboda an samu faruwar fyade da lalata kananan yara guda 15 wanda suke tsakanin shekaru 2 zuwa 7 na haihuwa a jihar kuma babu abinda ya faru ga wadanda suka aikata wannan laifi.

Gbazua ta ce lalacin da a ka yiwa 'yar shekaru 14 ta jihar Legas wanda sanadiyar haka ne ta rasa ranta ya assasa wannan zanga-zanga, kuma ta na gargadin gwamnatin jihar Benuwe da ta tabbatar da kwakkwaran mataki a kana ma su aikata wannan laifi kamar yadda gwamnatin tarayya ta bayar da dama tun shekarar 2015.

Don shawara ko bamu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku duba shafukanmu na sada zumunta a:

https://business.facebook.com/pg/naijcomhausa

https://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng

Tags: