Kaji abun da za'a yi wa gidan tarihin Sukur da Boko Haram ta Kona a jihar Adamawa?

Kaji abun da za'a yi wa gidan tarihin Sukur da Boko Haram ta Kona a jihar Adamawa?

Hukumar nan ta gwamnatin tarayya dake kula da ababen tarihi da wurare watau NCMM a takaice ta bayyana cewa ta soma shiri-shiren don gyara gidan nan mai dadadden tarihi na garin Sukur a jihar Adamawa da kungiyar Boko Haram ta lalata.

Alhaji Yusuf Usman wanda yake zaman shugaban hukumar shine ya bayar da tabbacin hakan a garin Abuja da yake fira da yan jarida a jiya litinin.

Kaji abun da za'a yi wa gidan tarihin Sukur da Boko Haram ta Kona a jihar Adamawa?
Kaji abun da za'a yi wa gidan tarihin Sukur da Boko Haram ta Kona a jihar Adamawa?

Legit.ng ta samu labarin cewa Alhaji Yusuf Usman din ya kuma kara da cewa gyaran da hukumar tasu zata yi zai hada da na jihar Osun dake a garin Osogbo.

Ya kuma mika godiyarsa ga hukumar UNESCO da ta yi alkawarin tallafa wa gwamantin Najeriya da gyare- gyaren gidajen tarihin kasar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng