Yadda na kashe mijina tare da taimakon abokina – Inji Uwargida

Yadda na kashe mijina tare da taimakon abokina – Inji Uwargida

Wata mata, Omotayo Salawudeen ta bayyana yadda ta hada baki da wani abokinta Dolapo Oladapo suka kashe mijinta mai suna Alhaji Hakeem Salawudeen.

Legit.ng ta ruwaito yansandan jihar Osun sun samu nasarar cafke matar tare da abokin aika aikan nata, inda ta bayyana ma yan Jarida cewa a daren da zata kashe mijin nata, sai da suka yi rayuwar aure.

KU KARANTA: An miƙa koke ga jam’iyyar PDP akan lallai ta hukunta Sanata Sheriff

“Ni na gayyato Dolapo yazo ya kashe mijina, shekaru 17 muka yi dashi muna tare, kuma yayan mu 3, a gaskiya ban san abinda mijina yayi min ba, bai taba bata min rai ba, don haka nayi nadamar abin dana aikata.” Inji ta

Yadda na kashe mijina tare da taimakon abokina – Inji Uwargida
Matar da abokin aikin nata

Shima abokin matar, Oladapo, ya tabbatar ma yan jaridu cewa shi da kansa ya daba ma Alhji Hakeem wuka, bayan matar tasa ta rufe masa fuska da pillow, Oladapo ya bayyana cewa ya aikata hakan ne bayan matar tayi masa alkawarin zata bashi duk abinda ya bukata idan ya yar da bukatar ta.

Yadda na kashe mijina tare da taimakon abokina – Inji Uwargida
Matar da Abokin aika aika

Shima kwamishinan yansandan jihar ya tabbatar da faruwar lamarin, inda yace sun fara gudanar da bincike, kuma zasu mikasu ga kotu da zarar sun kammala binciken.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.ng

Taron PDP a Abuja:

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng

Tags: