Babbar magana! Yan asalin garin Abuja sun yi kazamar zanga-zanga

Babbar magana! Yan asalin garin Abuja sun yi kazamar zanga-zanga

Wasu gungun matasa da tsaffi mata da maza da sukayi ikrarin cewa sune yan asalin garin Abuja sun gudanar da wata zanga-zangar lumana a birnin tarayya na Abuja.

Yan asalin na Abuja sun yi zanga-zangar ne domin mika bukatar su ga gwamnatin tarayya wajen cewa suma suna so su rika zaben Gwaman kamar kowace jiha dake a kasar.

Legit.ng ta samu labarin cewa matasan da suka yi wannan gangamin sunyi shi ne a karkashin wata kungiyar su da suka sawa suna Inhabitants Development Association of Abuja (OIDA) a turance.

Babbar magana! Yan asalin garin Abuja sun yi kazamar zanga-zanga
Babbar magana! Yan asalin garin Abuja sun yi kazamar zanga-zanga

A yayin zanga zangar shugaban kungiyar Danladi Jeji yayi bayani mai tsawo inda kuma yayi kira ga gwamnatin tarayya da ta basu dama su rika zaben su don gwamanati bata tabuka masu komai.

Shugaban yayi alkawarin cigaba da fafutukar ganin an ceto yan asalin birnin ta hanyoyin da kundin tsarin mulkin kasa ya amince dasu.

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng