WAEC za ta saki sakamakon jarrabawar WASSCE a ranar Laraba

WAEC za ta saki sakamakon jarrabawar WASSCE a ranar Laraba

- WAEC ta ce zata saki sakamakon WASSCE na 2017 a ranar Laraba mai zuwa

- Hukumar ta bayyana cewa nan da ranar Laraba za ta saki sakamakon WASSCE na 2017

- Hukumar tace ta kirkiro 'Project 60' don inganta sashen ilimi

WAEC za ta saki sakamakon jarrabawar WASSCE na 2017 a ranar Laraba mai zuwa, 19 ga watan Yuli ko kafin ranar.

WAEC ta wallafa hakan ne a shafinta ta Facebook inda ta bayyana cewa nan da ranar Laraba za ta saki sakamakon.

Hukumar ta ce sake sakamakon jarrabawar a cikin gajerar lokacin wani bangare ne na WAEC ta sabon dabarun wanda aka sani da'Project 60'.

WAEC za ta saki sakamakon jarrabawar WASSCE a ranar Laraba
Ofishin WAEC

Hukumar tace ta kirkiro 'Project 60' don inganta sashen ilimi.

KU KARANTA: An gano wasu azuzuwan ƙasa a Zamfara inda ɗalibai ke ɗaukan darasi (HOTUNA)

Legit.ng ta ruwaito a watannin baya cewa an yi zaman jarrabawar a ranar Litinin, 27 ga watan Maris kuma ƙare a ranar 3 ga watan Mayu 2017.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng