Wani masanin littafin injila ya yi ikirarin cewa an kirkiri labarin Yesu Almasihu ne don a mulki talakawa

Wani masanin littafin injila ya yi ikirarin cewa an kirkiri labarin Yesu Almasihu ne don a mulki talakawa

- Joseph Atwill ya yi ikirarin cewa labarin Yesu Almasihu jabu ne

- Daular Roma ta kirkire shi don ta mulki talakawa ne, ya yi ikirari

Wani masanin littafin injila a kasar Amurka ya yi ikirarin cewa dukkan labarin Yesu Almasihu ya kasance kirkiraren labari.

Da yake rubutu a shafinsa na yanar gizo, Joseph Atwill ya yi ikirarin cewa daular Roma tayi amfani da labarin a matsayin jabu da aka shirya don mulkar talakawa.

Ya rubuta: “Ana iya kallon addinin Kirista a matsayin addini, amma zancen gaskiya an gina ta ne sannan kuma akayi amfani da ita a matsayin tsari na mulkar zuciya domin a samar da bayi da suka yarda da cewan Allah ne ke bautar da su.”

Wani masanin littafin injila ya yi ikirarin cewa an kirkiri labarin Yesu Almasihu ne don a mulki talakawa
Masanin littafin injila Joseph Atwill. Hoto: covertmessiah.com

A cewar Atwill daular Roma ne suka kirkiri labarin ne kawai domin su mulki mutane sannan su samar da Karin bayi.

Kalli Atwill a yayinda yake bayyana kudirin sa a cikin wannan bidiyo:

Ku same a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng