HOTUNAN yayinda gawar Danmasanin Kano ta isa jihar Kano

HOTUNAN yayinda gawar Danmasanin Kano ta isa jihar Kano

- Gawar Danmasanin Kano, Alhaji Yusuf Maitama Sule ya isa jihar Kano

- Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje tare da sauran manyan gwamnati ne suka tarbi gawar

- An karbi gawar Marigayin a sansanin jiragen sojojin sama dake Kano

Rahotanni sun kawo cewa gawar Danmasaini Kano kuma tsohon ministan Najeriya, Alhaji Yusuf Maitama Sule ya isa jihar Kano.

A dazu ne Legit.ng ta samu labarin isar gawar Danmasanin Kano da ya rasu a ranar Litinin, 3 ga watan Yuli a kasar Masar babban birnin tarayya Abuja.

Shugaban ma’aikata na tarayya, Abba Kyari, ne ya karbi gawar a ranar Talata, 4 ga watan Yuli tare da shugaban majalisar dattawa, Bukola Saraki wanda ya jagoranci tawagar gwamnatin tarayya zuwa jana’izar Danmasanin Kano.

KU KARANTA KUMA: Za’ayi jana’izar Danmasanin Kano a yau Talata da Misalin Karfe hudu

Jirgin dake dauke da gawar ya iso da misalin karfe 1:54 na rana.

A yanzu dai gwamnan jihar Kano, Alhaji Umar Ganduje, tare da manyan jami'an gwamnatin tarayya da kuma na jiha suka karbi gawar Marigayin a sansanin jiragen sojojin sama dake Kano.

Ga hotunan a kasa:

HOTUNAN yayinda gawar Danmasanin Kano ta isa jihar Kano
HOTUNAN yayinda gawar Danmasanin Kano ta isa jihar Kano Hoto: daga shafin Rariya

HOTUNAN yayinda gawar Danmasanin Kano ta isa jihar Kano
Manyan masu fada sun taru don karban gawar Hoto: daga shafin Rariya

HOTUNAN yayinda gawar Danmasanin Kano ta isa jihar Kano
An karbi gawar Marigayin a sansanin jiragen sojojin sama dake Kano Hoto: daga shafin Rariya

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng