Abin dariya kuma abin tausayi, yadda wani dan bas da fasinja suka daku da juna har cikin lambatu (Hotuna)

Abin dariya kuma abin tausayi, yadda wani dan bas da fasinja suka daku da juna har cikin lambatu (Hotuna)

- Fada ta kaure tsakani wani dan bas da fasinjan da ke cikin motan kan canji

- Mutanen biyu sun fafata har suka sami kansu cikin lambatu

- Sauran fasinjojin motar basu dakatar da fadan ba

Wani dan bas da fasinja suna takaman nuna gwaninta tsakanin su kamar yadda suka fafata da juna a kan kudi a bainar jama'a a Legas. Da alama cewa sararin da suke fadan bai ishe su ba sai kawai suka tutsar cikin wani lambatu a gaban fasinjojin jikin motar da kuma masu wucewa.

Legit.ng ta ruwaito cewa abin dariya a nan shine sauran fasinjoji wadanda ke kallon yadda fadan zai kasance sun ki dakatar da mutanen biyu kamar yadda suka ci gaba da fafatawa har cikin lambatu har suka samu gajiya.

KU KARANTA: Bayan El-Rufa’I ya alanta umurnin damke su, kungiyar matasan arewa sun shiga ganawa

Fafatawa tsakanin ‘yan bas dai da kuma fasinjoji a Legas ba sabuwar abu ba ce, abu ne dake faruwa yau da kulum. Abin mamaki a nan shine gaddama a kan kudi naira biyar kacal zai iya kai ku dare idan aka din ta faru tsakanin ku, don ba zasu taba yafewa ba, zai de kai ka bar musu.

Abin dariya kuma abin tausayi, yaddda wani dan bas da fasinja suka daku da juna har cikin lambatu (Hotuna)
Yaddda wani dan bas da fasinja suka daku da juna har cikin lambatu

Abin dariya kuma abin tausayi, yaddda wani dan bas da fasinja suka daku da juna har cikin lambatu (Hotuna)
Da farko dai fasinjojin cikin motar sun zuba masu ido har zai da suka kai cikin lambatu

Abin dariya kuma abin tausayi, yaddda wani dan bas da fasinja suka daku da juna har cikin lambatu (Hotuna)
Da alamu dai mutanen sun gaji da fadan

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Na rasa yara 4 a cikin rushe-rushen gidajen mu da gwamnatin jihar Legas ta yi, a cewar wata mata a cikin wannan bidiyo

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng