Hattara! Kunji yadda ake safarar mutanen arewa zuwa kasashen waje?

Hattara! Kunji yadda ake safarar mutanen arewa zuwa kasashen waje?

Safarar mutane ya dauki wani sabon salo a arewacin Najeriya inda kamfanoni ke shiryawa mutane zuwa kasashe kamar Saudiya domin su yi aiki a gidajen Larabawa da zummar fita daga kuncin rayuwa da suke fama da ita a Najeriya.

Joli Oka Donli daraktar hukumar hana safarar mutane ta Najeriya tace ta samu labarin kamfanoni na safarar mutane zuwa Saudiya da wasu kasashen Larabawa kuma tace ta tura rahoton wa bangaren dake sa ido da binciken lamarin.

Legit.ng ta samu labarin cewa inji Joli Donli ana gudanar da bincike akan batun saboda haka tace ba zata yi magana a kai ba sai an kammala binciken. Amma ta jawo hankalin jama'a cewa su a hukumance basu ba kowa iznin yayi safarar 'ya'yan mutane zuwa kowace kasa ko kasashen Larabawa ba.

Hattara! Kunji yadda ake safarar tsala-tsalan matan arewa zuwa kasashen waje?
Hattara! Kunji yadda ake safarar mutanen arewa zuwa kasashen waje?

Wani likitan asibiti dake Abuja da suke tantance lafiyar wadanda ake safarar zuwa kasashen Larabawa yace abun akwai ban tsoro. Yace ana kawo yaran cikin motoci cike makil, maza da mata. Yanzu ma kusan gaba daya mata ake debowa a kawosu domin tantance lafiyarsu.

Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng

Tags: