Gada ya fadi a jihar Niger (HOTUNA)

Gada ya fadi a jihar Niger (HOTUNA)

Wani gada ya fadi a kauyen Gidan Mai dake hanyar Mokwa-Makera sakamakon ruwan sama da aka sharara kamar da bakin kwarya. Wannan ya hana motoci tafiya daga bangarorin guda biyu.

Hukumar dake kare afkuwar hadurra ta Najeriya (FRSC), Mokwa, ta saki hotunan gadar da ya rufta a jihar a shafinta na Facebook.

Babu shakka faduwar gadar zai shafi kaiwa da komowa a ciki da wajen garin.

Ga hotunan gadar da ya fadi a kasa:

Gada ya fadi a jihar Niger (HOTUNA)
Gada ya fadi a jihar Niger

Gada ya fadi a jihar Niger (HOTUNA)
Gadar ya rufta ne a kauyen gidan Mai

Gada ya fadi a jihar Niger (HOTUNA)
A yanzu motoci ba su tafiya daga bangarorin biyu

Gada ya fadi a jihar Niger (HOTUNA)
Gadar ya rufta ne sakamakon ruwan sama da aka sheka kamar da bakin kwarya

A baya Legit.ng ta rahoto cewa hukumar FRSC sun bayyana cewa zasu bar hanyoyin jiha a Lagas kamar yadda gwamnan jihar, Akinwumi Ambode ya bukata.

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng