Buhari ne zai kai Najeriya ga ci, inji Sarkin Auchi ta jihar Edo

Buhari ne zai kai Najeriya ga ci, inji Sarkin Auchi ta jihar Edo

- Ana yabawa da mulkin Buhari a cikarsa shekaru biyu a kan mulki

- Buhari na shan suka daga wasu bangarori na kasar nan

- Sarkin Auchi ya yaba wa shugaba Buhari

A cikarsu shekaru biyu a kan mulki, shugaba Buhari ya sami yabo daga sarkin Auchin jihar Edo, mai martaba Sarki Alh. Aliru Momoh Ikelebe na III, inda yace kuncin da aka sha a wannan mulkin gini ne na abubuwan alheeri wadanda za'a girba nan gaba.

Otarun Auchin yace Buhari nayi wa kasar nan tanadi mai-kyau ne, kuma ya kawo canji a kasa. Ya fadi hakan ne a lokacin ziyarar gwaman jihar na APC da keyi ta shan ruwan azumi a fadarsa.

Buhari ne zai kai Najeriya ga gaci, inji Sarkin Auchi ta jihar Edo
Buhari ne zai kai Najeriya ga gaci, inji Sarkin Auchi ta jihar Edo

Ziyarar ta hada da mataimakin gwamnan jihar Malam Philip Shuaibu, a yayin shan ruwa da sarakunan gargajiya na yankin.

'Shugaba Buhari ya kawo ci gaba da chanji kasar nan, kuma ma duk inda yaje a kasashen waje, sai san barka da yake sha da tarba mai kyau'.

Ya kuma yi wa shugaban fatan nasara da karin lafiya.

Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng