Shugabannin kasa da su ka fi kowa tsufa a Afrika (Ina matsayin Shugaba Buhari)

Shugabannin kasa da su ka fi kowa tsufa a Afrika (Ina matsayin Shugaba Buhari)

– A Nahiyar Afrika dai ana buga wani irin mulki

– Shugaban kasar Zimababwe Mugabe yana da shekaru fiye da 90

– Shugaban Najeriya Buhari kuwa ya fi shekara 73

Shugaba Muhammadu Buhari bai cikin shugabannin 10 da su ka fi tsufa a Afrika duk da kuwa ya zarce shekaru 70 a Duniya don kuwa akwai manyan sa.

Shugabannin kasa da su ka fi kowa tsufa a Afrika (Ina matsayin Shugaba Buhari)
Shugaban kasar Najeriya Muhammadu Buhari

1. Robert Mugabe

Shugabannin kasa da su ka fi kowa tsufa a Afrika (Ina matsayin Shugaba Buhari)
Shugaba Mugabe ya fi kowa tsufa a Afrika

Shekarun shugaba Robert Mugabe na kasar Zimbabwe 93 a Duniya ke nan duk Afrika babu shugaban da ya kai sa tsufa da kuma dadewa a Ofis watau shekaru 40.

2. Beji Essebsi

Shugaban kasar na Tunisia ya haura shekaru 90 shi ma a Duniya wanda ya zo na biyu a jerin shugabannin da su ka sha miya.

3. Paul Biya

Shugabannin kasa da su ka fi kowa tsufa a Afrika (Ina matsayin Shugaba Buhari)
Shugaba Biya na kasar Kamaru

Shugaba Biya na nan Makwabtan Najeriya watau kasar Kamaru ya zarce shekara 83 a Duniya kuma har yanzu ana damawa da shi.

4. Abdelaziz Bouteflika

Shugabannin kasa da su ka fi kowa tsufa a Afrika (Ina matsayin Shugaba Buhari)
Shugaban Kasar Algeria ya dade a Duniya

Shugaba Bouteflika na Algeria yana da shekaru 80 a Duniya kuma duk kasar Algeria babu shugaban kasar da ya kais a dadewa a mulki.

5. Ellen Johnson Sir-Leaf

Shugabannin kasa da su ka fi kowa tsufa a Afrika (Ina matsayin Shugaba Buhari)
Shugaba Sir-leaf ta Kasar Liberia

Tana cikin shugabannin kasa mata da ake da su a Duniya, Shugaba Ellen Johnson ta Kasar Liberia tana da shekaru 78 a Duniya.

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Yadda farashin kaya su ka canza bayan dawowar Buhari

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng