Yan Najeriya ba zamu samu labarin Buhari daga bakinmu ba – Garba Shehu
-Mai magana da yawun shugaban kasa, Garba Shehu, yayi hira da yan jarida
-Yace bai tunanin zai je Landan duba shugaba Buhari
Shugaba Muhammadu Buhari ya koma birnin Landan ranan Lahadi, 7 ga watan Mayu domin jinyarsa amma bai bayar a takamamman ranan da zai dawo ba.
Mai magana da yawun shugaban kasa Muhammadu Buhari, Garba Shehu, ya bayyana cewa su kansu makusantan Buhari sai dais u samu labari daga masu jinyan shi.
Legit.ng ta bada rahoton cewa shugaban kasa ya tafi Landan domin ganin likita kamar yadda ya bayyanawa yan Najeriya kafin yanzu.
![Yan Najeriya ba zamu samu labarin Buhari daga bakinmu ba – Garba Shehu Yan Najeriya ba zamu samu labarin Buhari daga bakinmu ba – Garba Shehu](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt28b2sf19t9t.jpeg?v=1)
Garba Shehu wanda yayi wannan bayani a wata hiran tashar Channels Tv yace ba zai je Landan domin ganin shugaban kasa ba amma wadanda ke tare da shi zasu dinga basu labarin abinda ke faruwa.
KU KARANTA: Manufarmu daya da shugaba Buhari - Amurka
“Ba tunanin zan je, ina tunanin shugaban kasan na bukatan zama da likitocina har ya samu lafiya.”
Kafin yanzu, shugaba Buhari yayi kwanaki a Landan kafin ya dawo ranan 10 ga watan Maris, 2017.
https://web.facebook.com/naijcomhausa/#
https://twitter.com/naijcomhausa
Asali: Legit.ng