Gwamna Ganduje ya kai wa mahaifin sanata Kwankwaso ziyara (Hotuna)

Gwamna Ganduje ya kai wa mahaifin sanata Kwankwaso ziyara (Hotuna)

- Gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje ya ziyarci mahaifiyar sanata Musa Kwankwaso a fadarsa da ke garin Madobi

- Gwamnan ya yi wannan ziyara ne bayan ta’aziyar mahaifiyar shugaban karamar hukumar Madobi

Mai Girma Gwamna jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje ya kai ziyara wajen Hakimin Madobi kuma Majidadin Kano Alhaji Musa Kwankwaso a fadar sa dake garin Madobi.

Kamar yadda Legit.ng ke da labari, gwamna Ganduje ya je garin Madobi ne domin ta'aziyar rasuwar mahaifiyar shugaban karamar hukumar Madobi.

KU KARANTA KUMA: Gwamnonin APC na yunkurin daukar nauyin musanyar sabon dan takarar jam'iyyar don takarar 2019.

Gwamna Ganduje ya kai wa mahaifin sanata Kwankwaso ziyara (Hotuna)
Alhaji Musa Kwankwaso ya yi maraba da gwamna Abdullahi Ganduje

Za a iya tunawa dai cewa gwamna Ganduje ya kasance mataimakin Rabiu Kwankwaso a lokacin da yake gwamnan jihar, amma jim kadan bayan rantsar da Ganduje a matsayin gwamna sai rashin jituwa ya shiga tsakanin shugaban biyu.

Gwamna Ganduje ya kai wa mahaifin sanata Kwankwaso ziyara (Hotuna)
Gwamna Ganduje da tawagarsa a fadar Hakimin Madobi kuma Majidadin Kano Alhaji Musa Kwankwaso

Har yanzu dai samman doya da manja suke yi da juna, inda rahotannin baya-baya nan ke nuna cewa tsohon gwamnan na shirin sheka daga jam’iyyar mai mulki APC zuwa PDP.

Gwamna Ganduje ya kai wa mahaifin sanata Kwankwaso ziyara (Hotuna)
Gwamna Ganduje na gaisawa da jama'a a garin Madobi

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Ku kali yadda gwamnan jihar Ogun ke tukar uwargidansa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng

Tags: