Sule Lamido yana fuskanta shari’a a Dutse, babban birnin jihar Jigawa

Sule Lamido yana fuskanta shari’a a Dutse, babban birnin jihar Jigawa

- An tafi da tsararren tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido Dutse, wato babban birnin jihar domin fuskantar hukunci sakamakon furucin da yayi na rashin ladabi

- Yan sandar zone 1 ta tsare tsohon ministan harkokin wajen Najeriya, Lamido a Asabar din da ta wuce biyowa bayan korafi da gwamnatin jihar Jigawa tayi

Majiya daga jami’an tsaro a zone 1 sun fadawa Legit.ng cewa yansanda daukeda manya-manyan makamai ne suka raka dan gaban goshin PDP a tafiyar kimanin awa daya a motar Toyota Hilux zuwa makwantarsa a babban birnin jihar.

Wani daga jami’an tsaron a tafiyar tasu zuwa dutse ya sirrantawa Legit.ng akan yarjejeniyar kar a fadi sunansa cewa sun bar kano zuwa dutse a kimanin karfe 5.30 na safe.

KU KARANTA: 2019: Gwamnonin Jihohi 4 da sai sun yi da gaske

Ya kara da cewa a yanzu haka da nake maganar nan muna dutse domin tsaretsaren daya dace ta kara gano cewa an tsinkayar das u jami’an tsaron cewa magoya bayan shi tsohon gwamnan na iya tada zangazanga.

Sule Lamido yana fuskanta shari’a a Dutse, babban birnin jihar Jigawa
Sule Lamido, tsohon gwamnan jihar Jigawa

A tabbatar da hakan wakilin yansandan Zone 1, Sambo Dasuki yace, Lamido na Dutse ne domin fuskantar tuhuma.

Akwai rade-raden take cewa wanda wani tsohon gwamnan yana da aniyyar tsaya takarar shugaban kasa a shekarar 2019.

Ku biyo mu anan https://www.facebook.com/naijcomhausa/

Da anan https://twitter.com/naijcomhausa

Bidiyon shugaban kungiyar IPOB

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng

Tags: