Wannan abu da me yayi kama: Gwamna ya tikawa wata ciki
– Akwai kishin-kishin din cewa wani Gwamna yayi wata mai hidimar kasa ciki
– Yanzu haka an yi kasar waje da wannan Budurwa
– Tana dauke da juna biyun wannan Gwamna
Ko ina Duniya za ta damu Jama’a?
Wani Gwamna ne dai ya jibgawa wata mai bautar kasa a Jihar sa ciki.
Yanzu an yi kasar waje da wannan baiwar Allah.
![Wannan abu da me yayi kama: Gwamna ya tikawa wata ciki Wannan abu da me yayi kama: Gwamna ya tikawa wata ciki](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt6kfgq5lb37m.jpeg?v=1)
Legit.ng na samun labari daga wata mai suna Stella Dimokokorkus cewa wani Gwamnan Najeriya ya dirkawa wata Budurwa da ta ke aikin hidimar kasa a Jihar sa ciki. Stella dai tace ba za ta kama suna ba.
KU KARANTA: Ina nan zan tona asiri Inji Jonathan
![Wannan abu da me yayi kama: Gwamna ya tikawa wata ciki Wannan abu da me yayi kama: Gwamna ya tikawa wata ciki](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt2tiimdqdeirg.jpeg?v=1)
Dimokokorkus ta bayyana cewa Budurwar tana yin aikin hidimar kasar ne a gidan Gwamnati wanda da aka je aka dawo Gwamnan yayi mata ciki. Kai karshen takaitawa dai wannan Budurwa ta haifi ‘yan biyu a kasar waje.
A can kasar wajen kuma Kungiyar wasan kwallon kafa ta Manchester United da ke Kasar Ingila tayi makokin ‘Yan Najeriya da su ka rasu wajen kallon wasan Kungiyar a Garin Kalaba.
Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa Ko a http://twitter.com/naijcomhausa
Asali: Legit.ng