Hukumar INEC ta tsai da ranar sake zabe a jihar Katsina

Hukumar INEC ta tsai da ranar sake zabe a jihar Katsina

- Hukumar zabe ta shiyar Katsina ta ce ta tsai da ranar 20 ga watan Mayu a matsayin ranar sake zaben mazabar Mashi / Dutsi ta tarayya

- Kura ya ce jam'iyyun siyasa za su gudanar da zaben fitar da dan takara tsakanin watan Mayu 1 zuwa 4, 2017

- Kura ya tabbatar da cewa za a fara gangamin kamfen daga watan Mayu 5 da kuma kawo karshe a ranar 19 na watan

Hukumar zabe mai zaman kansa (INEC) ta tsai da ranar 20 ga watan Mayu a matsayin ranar sake zaben mazabar Mashi / Dutsi ta tarayya a Jihar Katsina.

Legit.ng ta ruwaito cewa za a yi wannan zaben cika gurubin mazabar ne sanadiyar rasuwar dan majalisar mai wakiltar mazabar, Alhaji Sani Bello a ranar 15 ga watan Fabrairu, 2017.

Jami’in hukumar, Mista Yunusa Kura ya bayyana haka a ranar Laraba, 26 ga watan Afrilu a Katsina a lokacin wata taron ruwa da tsaki a jihar.

KU KARANTA KUMA: Har yanzu babu kasafin kudin wannan shekarar a Najeriya

Kura ya ce a na sa ran jam'iyyun siyasa za su gudanar da zaben fitar da dan takara tsakanin watan Mayu 1 zuwa 4, 2017.

Ya ce jam'iyyun siyasa za su fara gangamin kamfen daga watan Mayu 5 da kuma kawo karshe a ranar 19 na watan.

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Yadda hukumar EFCC ta gurfanar da wasu jami'in hukumar zaben na INEC a kotu a cikin wannan bidiyo

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng

Tags: