Ban da ni cikin wadanda aka jefa a Katsina - inji Honarable Aminu Tukur

Ban da ni cikin wadanda aka jefa a Katsina - inji Honarable Aminu Tukur

- Dan majalisa mai wakiltan Bakori da Danja jihar Katsina, Amiru Tukur yace bashi acikin wadanda suka sha ruwan duwatsu a taron jam’iyyar da akayi a garin Funtua.

- Amiru ya sanar mana da haka ne da yake zantawa da wakili majiyar mu na majalisar Wakilai Nasiru Ayitoro.

“Babu wanda ya kai mini hari a wannan taro, duk da cewa naji wai an kai ma wasu manyan baki hari a taron.

“Ni ma ji nayi cewa wai an kai wannan hare-hare a lokacin da abokanai na da ‘Yan’uwa suke ta kira na domin yi mini jaje cewa wai sunji an har-harbe ni. Na gaya musu ba haka bane domin ni bana wajen taron a lokacin da hakan ya faru. Kamar yadda ka ganni yanzu haka lafiya na lau. Kuma ka sani cewa wannan tashin hakali ya faru ne a Funtua kuma ni ina wakiltan Bakori ne da Danja."

Legit.ng ta samu labarin cewa Sanata mai wakiltan Katsina ta Kudu da dan majalisan da ke wakiltan Kananan hukumomin Bakori da Danja a majalisar wakilai sun sha da kyar a taron jam’iyyar APC da akayi a garin Funtua.

Kamfanin dillancin labarai ta rahoto cewa jami’an ‘yan sanda ne suka kawo musu dauki da ya hada da tawagar gwamnan jihar Aminu Bello Masari.

Ban da ni cikin wadanda aka jefa a Katsina - inji Honarable Aminu Tukur
Ban da ni cikin wadanda aka jefa a Katsina - inji Honarable Aminu Tukur

Sun sha ruwan duwatsu da takalma a harin inda sai da akayi amfani da barkonun tsohuwa kafin aka samu shawo kan matasan.

KU KARANTA: Yan Boko Haram sun kai wa sojojin Najeriya harin ba zata

Gwamna Masari da sanata Abu Ibrahim suna halartar taron karban wasu ‘Ya’yan jam’iyyun PDP, APGA da PDM ne da suke canza sheka zuwa jam’iyyar APC.

Ba’a dade da fara taron ba kwatsam sai matasa suka fara ihun “Ba ma son Abu Ibrahim ba ma so” sai suka fara jefar bakin da duwatsu da takalma.

Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

Ga wani matashi nan na bada ra'ayn sa game da yan siyasar mu

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng

Tags: