Madalla! Sojoji a Nijer sun samu nasarar kashe yan Boko Haram 57

Madalla! Sojoji a Nijer sun samu nasarar kashe yan Boko Haram 57

- Wata majiyar tsaro a Nijar ta ce sojojin kasar sun kashe mayakan Boko Haram akalla 57 a wata musayar wuta da suka yi a kusa da garin Gueskerou

- Garin yana cikin Jihar Diffa yankin kudu masu gabashi da ke kan iyaka da Najeriya.

Legit.ng ta samu labarin cewa akwai babban kwamandan Boko Haram daga cikin mayakan da aka kashe, kamar yadda majiyar sojin ta tabbatarwa kamfanin dillacin labaran Faransa.

Sojojin Nijar sun yi nasarar fatattakar yan Boko Haram ne bayan sun shigo garin cikin mota da Babura a ranar Lahadi.

Majiyar da ta tabbatar da labarin ta ce akwai sojoji da dama da suka samu rauni a musayar wutar.

Sojoji a Nijer sun samu nasarar kashe yan Boko Haram 57
Sojoji a Nijer sun samu nasarar kashe yan Boko Haram 57

Sannan Sojojin sun yi nasarar kwato tarin makamai daga hannun mayakan na Boko Haram.

KU KARANTA: Anyi mummunan artabu tsakanin yan sanda da yan shi'a

Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

Nan ma dai wasu mutane ne da suka tsere wa rikicin Boko haram

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng