Da kyau: Malaman Najeriya sun shiga tarihi a Duniya

Da kyau: Malaman Najeriya sun shiga tarihi a Duniya

– Malaman Jami’ar Bayero ta Kano sun shiga cikin littafan tarihi

– An jero Malaman Jami’ar cikin wadanda su ka fi kowa bincike a Duniya

– Da alamu Jami’ar na nema ta ciri tuta a Afrika da ma Duniya

Da kyau: Malaman Najeriya sun shiga tarihi a Duniya
Ministan Ilmi Adamu Adamu

Legit.ng ta samu labarin cewa wasu Malamai daga Jami’ar Bayero ta Kano sun shiga sahun Malaman da su ka fi kowa nazari da bincike a Duniya a halin yanzu. Wannan dai ba karamin abu ba ne musamman a wannan yanki na Duniya.

Malaman da su ka yi fice sune:

1. Farfesa Mahmud Umar Sani

2. Farfesa Muhammad Ajiya

3. Dr. Nuraddeen Magaji

4. Farfesa Yusuf M. Adamu

5. Dr. Ahmed A. Maiyaki

6. Dr. Umar Ibrahim Gaya

7. Dr. Dahiru Sani Shu’aibu

8. Dr. Muhammadu Yusuf Waziri

9. Farfesa Bashir Ali

10. Dr. Muhammad Shu’aibu Abubakar

KU KARANTA: Malamai za su shiga yajin aiki

Da kyau: Malaman Najeriya sun shiga tarihi a Duniya
Shugaban Jami'ar Bayero ta Kano

Malaman da su ka yi fice a fannoni irin su lissafi, ilmin sinadarai, bangaren fasaha da sauran su sun shigo cikin sahun wadanda su ka fi kowa nazari a bana wanda a Afrika Najeriya na cikin wadanda aka dauka. Mun samu wannan bayani ne daga wata Mujallar Jami’ar.

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Ga wata mata ita kuma da inda tayi fice

Asali: Legit.ng

Authors:
Muhammad Malumfashi avatar

Muhammad Malumfashi (Hausa writer) M. Malumfashi ya samu Digirin farko a ilmin komfuta a ABU Zaria. Baya ga haka ya yi Digirgir a fannin kula da bayanai da wani Digirgir a ilmin aikin jarida duk daga jami'ar. Malumfashi ya kan kawo labaran siyasa, addini, wasanni da al’ada. Ya halarci taron karawa juna sani iri-iri. Imel: muhammad.malumfashi@corp.legit.ng