Abubakar Shekau na raye - Gwamnatin tarayya

Abubakar Shekau na raye - Gwamnatin tarayya

Daga karshe gwamnatin tarayya ta amince da cewan shugaban kungiyar Boko Haram, Abubakar Shekau na raye har yanzu.

Abubakar Shekau na raye - Gwamnatin tarayya
Gwamnatin tarayya ta ayarda da cewa Abubakar Shekau na raye

Ministan tsaro, Mansur Dan-Ali, ya bayyana hakan a ranar Talata, 28 ga watan Maris, jim kadan bayan ya gana da shugaban kasa Muhammadu Buhari kan ayyukan ma’aikatar sa a fadar shugaban kasa, Abuja.

Dan Ali yayi bayanin cewa kama shugaban yan ta’addan yayi ma hukumomin tsaro wahala saboda yan ta’addan na rufe fuska don boye kammaninsu da kuma dauke hankulan mutane, jaridar Punch ta ruwaito.

KU KARANTA KUMA: YANZU YANZU: Buhari ya tsige daraktocin tarayya 5

A halin da ake ciki, ministan ya bada tabbacin cewa za’a kama Shekau nan bada jimawa ba.

Yace duk wanda Allah yaba daman ziyartan dajin Sambisa zai san cewa an yi nasara a kan yan Boko Haram.

Legit.ng ta rahoto inda, Dan Ali ke yace hukumomin tsaro na kasar zasu ci gaba da mamaye dajin Sambisa, tsohon sansanin yan ta’addan, don gano inda Shekau yake.

“Na yarda da cewan komai lokaci ne. ya dauki kasar Amurka shekara bakwai zua goma kafin ta kama Bin Ladan. Don haka, zamu kama Shekau nan bada jimawa ba.

“An kakkabe hedkwatar yan ta’addan. Shi (Shekau) na neman hanyar gudu.

“Babu mamaki yana nan boye a bangare daya na dajin Sambisa wanda muka mamaye a yanzu.

“Mun bude gurin. Muna amfani da gurin a mastayin gurin horo. Injiniyoyin hukumar soji zasu bude hanyoyi sannan kuma zamu kewaye dajin don sanin inda Shekau yake,” cewar sa.

KU KARANTA KUMA: Ba za mu sake bari ‘Yan ta’adda su kwace wani yanki na kasar nan ba – Inji Buhari

Da aka tambaye shi kan dalilin da yasa gwamnati tayi ikirarin cewa an kashe Shekau a baya, ministan yace barda kammani da yan ta’addan keyi ne ya haifar da haka.

Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

Ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Bidiyon wata yarinya da aka ceto daga rikicin Boko Haram a Arewa maso gabashin kasa:

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng