Wayyo! Ana nema a kashe ni Inji Hadiza Bala Usman
Shugabar Hukumar NPA ta kasa ta koka inda take cewa wasu Jama’a na nema su ga bayan ta. A wannan makon ne dai Hajiya Hadiza Bala Usman tayi wannan kukan
![Wayyo! Ana nema a kashe ni Inji Hadiza Bala Usman Wayyo! Ana nema a kashe ni Inji Hadiza Bala Usman](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt2f5qo8vlcst.jpeg?v=1)
Hadiza Bala Usman mai shugabantar hukumar NPA masu kula da iyakokin ruwa ta bayyana cewa wasu na nema su batar da ita. Hajiya Hadiza ta bayyana wannan ne a shafin ta na Twitter a Ranar Laraba.
Hajiya Hadiza Bala tayi aiki da Gwamnan Jihar Kaduna Malam Nasir El-Rufa’i a matsayin shugaban Ma’aikatan gidan Gwamnati kafin shugaba Buhari ya nada ta shugabar Hukumar NPA na kasa.
KU KARANTA: Shugaba Buhari ya aika takarda kasar Ingila
![Wayyo! Ana nema a kashe ni Inji Hadiza Bala Usman Wayyo! Ana nema a kashe ni Inji Hadiza Bala Usman](https://cdn.legit.ng/images/1120/vllkyt76n8130vpa.jpeg?v=1)
Wata Jarida dai tayi ikirarin cewa shugabar ta NPA ta gana da wasu ‘Yan Jam’iyyar APC a baya. Sai dai tayi maza ta karyata wannan zargi inda tace za ta kai kara kotu. Tuni dai masu jaridar su ka nemi ayi masu afuwa amma tace sam sai a gaban Alkali don kuwa an bata mata suna.
Haka kuma Femi Falana wanda shararren Lauya ne a Najeriya ya bayyana cewa Majalisar dattawa na da damar bada umarni a kama Sakataren Gwamnatin kasar Babachir David Lawal. Falana yace doka ta ba Sanatocin wannan damar idan har Babachir bai hallara gaban ta ba.
Ku same mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa Ko a http://twitter.com/naijcomhausa
Asali: Legit.ng