Yan sanda sun damke masu garkuwa da mutane 3 (Hotuna)

Yan sanda sun damke masu garkuwa da mutane 3 (Hotuna)

- Hukumar yan sanda na kasa, a ranan Juma’a tace ta damke masu garkuwa da mutane 3 a zariya, jihar Kaduna

- Hukumar tayi ram da su ne bayan sun je wani aikin yin garkuwa a ranan Laraba, 15 ga watan Maris

Yan sanda sun damke masu garkuwa da mutane 3 (Hotuna)
Yan sanda sun damke masu garkuwa da mutane 3 (Hotuna)

A ranan Juma’a, 17 ga watan Maris, hukumar yan sanda tace ta damke yan garkuwa da mutane a garin Zariya, jihar Kaduna. Kakakin hukumar yan sanda,Jimoh Moshood yace masu garkuwa da mutanen sune: Nuhu Fulani, 32; Yahaya Muhammed, 26 da Aisha Bature, 23.

Moshood yace: “Masu garkuwa da mutanen sun kasance kan jerin sunayen wadanda ake nema. Yayin bincike, sun tona asirinsu cewa sune suke gudanar da sace-sace da kuma garkuwa da mutane a babban titin Zariya zuwa Kaduna.”

KU KARANTA: Naira ta takara daraja

Yan sanda sun damke masu garkuwa da mutane 3 (Hotuna)
Yan sanda sun damke masu garkuwa da mutane 3 (Hotuna)

Kana yace yan barandan sunyi bayani ga masu binciken yan sanda wasu rawa da suka taka wajen wasu laifuka a jihar.

" Kana wasu mutane sun gane su. Amma ana gudanar da bincike akansu da kuma sauran yan kungiyan da suka arce,”

Daga cikin abubuwan aka kwace a hannunsu sune AK 47, karamin bindiga, harsasai da waya Samsung S6.

An kama bindiga AK 47a cikin bayin wata Aisha wacce itace matar shugaban yan fashin.

https://www.facebook.com/naijcomhausa/#

https://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng