Gungun ýan bindiga da dama sun miƙa wuya ga sojoji a Zamfara, sun ajiye makamai masu yawa

Gungun ýan bindiga da dama sun miƙa wuya ga sojoji a Zamfara, sun ajiye makamai masu yawa

Wasu gungun yan bindiga tare da barayin shanu sun mika wuya tare da mika makamansu ga dakarun rundunar sojan kasa a jihar Zamfara, kamar yadda Kaakakin rundunar Sani Usman ya bayyana.

Gungun ýan bindiga da dama sun miƙa wuya ga sojoji a Zamfara, sun ajiye makamai masu yawa
Gungun ýan bindiga da dama sun miƙa wuya ga sojoji a Zamfara, sun ajiye makamai masu yawa

Birgediya janar SK Usman ya bayyana cewa tubabbun yan bindigan sun mika wuya ne biyo bayan wani shirin afuwa da gwamnatin jihar tare da hedikwatar runduna ta daya na Sojoji suka faro tun a shekarar 2016.

KU KARANTA: Shugaban ƙungiyar ta’addanci ‘Al-Shabab’ ya miƙa wuya ga gwamnatin ƙasar Somalia

Gungun ýan bindiga da dama sun miƙa wuya ga sojoji a Zamfara, sun ajiye makamai masu yawa
Gungun ýan bindiga da dama sun miƙa wuya ga sojoji a Zamfara, sun ajiye makamai masu yawa

Sanarwar tace: “A ranar Laraba 8 ga watan Maris 2017,wasu tubabbun yan bindiga tare da yan-sakai daga kauyen Ruwan Tofa, ‘Yar Galadima da Babban Doka dake karamar hukumar Maru, da wasu daga kauyen Danwaren na karamar hukumar Tsafe da kuma kauyen Mada dake karamar hukumar Husau sun mika dimbin miyagun makamai ga rundunar sojan kasa.

Gungun ýan bindiga da dama sun miƙa wuya ga sojoji a Zamfara, sun ajiye makamai masu yawa
Gungun ýan bindiga da dama sun miƙa wuya ga sojoji a Zamfara, sun ajiye makamai masu yawa

“Cikin makaman da suka mika akwai bindigun AK-47 guda 3, kananan bindigu guda 323, bindigan toka guda 1,169, bindigan revolver guda 54, bindiga mai baki biyu guda 22, sai kuma wasu bindigu masu baki uku guda 102.

Gungun ýan bindiga da dama sun miƙa wuya ga sojoji a Zamfara, sun ajiye makamai masu yawa
Gungun ýan bindiga da dama sun miƙa wuya ga sojoji a Zamfara, sun ajiye makamai masu yawa

“An mika makaman ne a hannun bataliya ta 223 a gaban wasu jami’an gwamnatin jihar tare da shuwagabannin hukumomin tsaro da dama. A yan watannin da suka gabata, an samu makamai sama da 1000 da aka mika su ga hukuma.”

Ku biyo mu a https://www.facebook.com/naijcomhausa

ko a http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng