Amina Mohammed ta yi magana mai mai ratsa jiki a jawabin ta na farko a majalisar dinkin duniya

Amina Mohammed ta yi magana mai mai ratsa jiki a jawabin ta na farko a majalisar dinkin duniya

Tsohuwar ministar muhallin Buhari daga jihar Adamawa kuma sabuwar mataimakiyar Sakatare Janar na majalisar dinkin duniya tayi wani dogon bayani mai rasta jini a jawabin ta na farko a majalisar.

Amina Mohammed ta yi magana mai mai ratsa jiki a jawabin ta na farko a majalisar dinkin duniya
Amina Mohammed ta yi magana mai mai ratsa jiki a jawabin ta na farko a majalisar dinkin duniya

An dai ruwaito cewar Amina Muhammad ta yi bayain ne mai cike da hikima da basira a cikin satin da ya gabata yayin da take shan rantsuwar kama aiki a majalisar.

A cikin jawabin nata, Amina Muhammad wadda ta fito daga arewacin Najeriya tace dole ne majalisar ta dinkin duniya ta shirya tsaf kuma tayi adalci idan dai har tana so a rika daratta ta.

KU KARANTA: Sabon sako daga Osinbajo

Hakama ta jinjinawa Sakataren na majalisar saboda yadda da yayi da ita yayin da kuma ta sha alwashin ba mara da kunya a aikin nata.

Mai karatu dai zai tuna cewa, Sakatare-Janar na majalisar dinkin duniya, Antonio Guterres, ya nada Ministar muhalli ta Najeriya Amina Mohammed a matsayin mataimakiyarsa.

Mista Guterres ya kuma nada wasu mata biyu a wasu manyan mukamai a majalisar.

Ku ci gaba da bin mu a Facebook: https://www.facebook.com/naijcomhausa da

Kuma Tuwita: http://twitter.com/naijcomhausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng